15/10/2023
MU CIGABA DA SANYA MUSULMAN FALASƊINU CIKIN ADDU'O'INMU.
Haƙiƙa suna matuƙar buƙatar addu'o'inmu da gaske ba tare da wasa ba, duk wani mutum mai imani kuma yake bibiyar abin da ke faruwa na wannan yaƙi na zalunci dake aukuwa tabbas zai tsinci kansa cikin wani irin yanayi na tausayawa da kukan zuci na zahiri da baɗini.
Musulmi ɗan'uwan Musulmi ne, akwai haƙƙi na musulunci ga duk halin da ɗan'uwanka musulmi ya kasance, idan ya kasance cikin farin ciki ka taya shi kayi masa fatan alkhairi, idan ya kasance cikin halin baƙin ciki ko damuwa ka jajanta masa kayi masa addu'ar neman yayewa.
Shin dame zamu taimakawa ƴan'uwanmu musulmai waɗanda s**a fuskanci wannan jarrabawa ta yaƙi da kisan gilla da ake yi musu? Taimakon da zamu iya yi musu kawai shi ne ADDU'A domin shi ne kawai abin da zamu iya sadaukar musu, mu roƙi ALLAH Ya basu nasara akan zalunci da Azzalumai.
Kada Addu'o'inmu ya tsaya kawai a ƙafafen sada zumunta, lallai wajibi ne mu jajirce da sanya ƴan'uwanmu a addu'a a dukkan wuraren Ibadodinmu.
Ya ALLAH kar ka bawa maƙiyanka dama akan masu kaɗaita ka da bauta, Ya ALLAH ka kare jini da dukiyoyin bayinka a falasɗin, Ya ALLAH ka ruguza Yahudawa da duk masu goya musu baya. Ya ALLAH idan laifi muka maka yasa ka jarrabi al'ummar falasɗin da kasancewa a cikin halin da suke ciki, Ya ALLAH ka yafe mana, kar ka k**a su da laifin wawayen cikinmu. Ya ALLAH mun ƙasƙantar da kawunanmu a gareka muna neman afuwarka da roƙa musu mafita daga wajenka. Maƙiyanka sunyi taron dangi akansu saboda kawai sunce kai kaɗai ne abun bauta, kuma Annabi Muhammad (ﷺ) bawanka ne kuma manzonka ne.
Ya ALLAH Wanda Ka tsaga kogi ga Annabi Musa da Rahamarka, Ka fitar da Annabi Yusuf daga kurkuku da Ikonka, Ka tseratar da Annabi Yunus daga cikin kifi da Tausayinka, Muna roƙonka ka tausayawa Mutanen GAZA (Palestine) ka sauƙar musu da rahamarKa 🤲