DARUL HAQ

DARUL HAQ MAHUTA

KEMA KINA IRIN WANNAN HALAYYAR IDAN KINA HAILA KO KUWA?Wasu mata da yawa suna sakaci. Da ibada lokacin da suke haila. Wl...
01/04/2026

KEMA KINA IRIN WANNAN HALAYYAR IDAN KINA HAILA KO KUWA?

Wasu mata da yawa suna sakaci. Da ibada lokacin da suke haila. Wllh wasu kaace sun bar musulunci ne idan suna haila. Wa,iya zubillahi, to mata kusani. Haila bata hana ibada. Abunda ya tabbata A' Shari,a , Mai haila take bari. Acikin ibada shine. Azumi da sallah , Azumi shi zata rama idan tayi tsarki. Sallah kuma wannan base ta rama ba, wata zatace to karatun ALQUR "ANI,FA? Shi karatun Al, Qur'Ani, malamai sunyi maganganu akanshi, jamhur na malamai sun tafi akan mace mai haila zata iya daukan wani sashi na Al Qur'Ani. Ta karan ta. An tambayi wani daga cikin magabata. Akace masa mace Mai haila zata iya karanta Al, Qur'Ani, acikin wayar ta,? Yace wannan babu laifi,. Zata iya.
Amma me yasa mata wasu daga cikinsu idan suna haila. Za kaga sun fita daga cikin rayuwar musulunci? To gsky wannan kuskure ne Sosai, kuma laifi ne, domun ba,a, hanaki AZKAR ba na safe da yanmaba. Ba,a, hanaki ki tashi gabda fitowar alfijir. Ki roki Allah ba kuma kiyi istigifari, domun ita kanta ADDU,AN ibada ce AZKAR , shima ibada ne, da sauran maka mantan wannan. To don Allah mata mu gyara wannan dabi,ar. Karki mutu ki hadu da Allah. Kina barin ibadun daba,a haramta maki ba idan kina haila, kuma yana daga cikin rashin wa,yau. Kiga mace ance ta bar sallah, tabar azumi, me makon wannan lokacin da aka bata, ta samu ta cikeshesu, da wasu ibadun, Amma kuma ake sakaci dasu, mu duba rayuwar matan (Annabi Muhammad. S,A,W, ba haka suke ba,. Mu duba rayuwar matan sahabbai. Suma ba haka suke ba,. To me yasa mu matan mu wasu daga cikinsu suke sakaci da hakan? Gaskiya wannan ba ,halin mumina bace. Shifa mumini. Idan wata ibada ta kubuce masa, bayan damuwa da zaiyi. Se kaga yana neman wata hanya. Da zai cike wancen Ibadan data kubuce masa,. To haka mumini yake. Don Allah yan uwa mata agyara wannan dabi,ar

Allah ubangiji ya bamu iKon gyarawa, ya sanya mu cikin. Ibadurrahman,. Amin

( naja'At Abbkr. Ummu taufeq ✍️✍️).

M,N

04/03/2026
ما هي فوائد قراءة سورة المائدة في رمضان؟قراءة سورة المائدة في رمضان لها العديد من الفوائد الروحية والتعبدية. إليك بعض ال...
03/03/2026

ما هي فوائد قراءة سورة المائدة في رمضان؟

قراءة سورة المائدة في رمضان لها العديد من الفوائد الروحية والتعبدية. إليك بعض الفوائد المذكورة في تفسير العلامة ابن عثيمين ¹:
- زيادة الإيمان والتقوى: سورة المائدة تشتمل على آيات تحث على تقوى الله ومراقبته، وتذكّر باليوم الآخر، مما يعزز الإيمان ويزيد من تقوى المؤمنين.
- الرضا بقضاء الله: السورة تذكر برضا الله عز وجل عن عباده الصالحين، وهذا يعزز الرضا بقضاء الله وزيادة الطاعة.
- الاهتمام بأعمال القلب: سورة المائدة تؤكد على أهمية أعمال القلب مثل الإيمان والمحبة والتوكل على الله، وتدعو إلى تطهير القلب من الشرك والنفاق.
- الحرص على العلم النافع: السورة تشير إلى أهمية العلم والتعلم، وتفسير القرآن الكريم، وضرورة اتباع طريق السلف الصالح.
- الابتعاد عن المعاصي: السورة تحذر من المعاصي وآثارها السيئة على الفرد والمجتمع، وتدعو إلى التوبة والاستغفار.
- التمسك بالدين: سورة المائدة تشدد على أهمية التمسك بالإسلام والالتزام بتعاليمه، وتدعو إلى الدعوة إلى الله بالحكمة والموعظة الحسنة.

بشكل عام، قراءة سورة المائدة في رمضان يمكن أن تكون وسيلة لتعزيز الروحانية وزيادة الوعي بدين الله، وتحفيز المسلم على الالتزام بتعاليم الإسلام.

(TAFIYA TA DIN DIN DIN)KABARI:. Shine matakin farko daga cikin matakan lahira,rami ne daga cikin ramukan wuta Dan gane d...
05/02/2026

(TAFIYA TA DIN DIN DIN)
KABARI:. Shine matakin farko daga cikin matakan lahira,rami ne daga cikin ramukan wuta Dan gane da kafirai da munafukai, Amma Dan gane da muminai, dausayi ne na aljannah. Kuma an ruwaito cewa ana yin azaba a cikinsa sakamakon wasu laifuka , daga cikinsu akwai: Rashin tsarkaka lokacin fitsari, da yada annamimanci da satar ganima kafin arabata da karya da barin sallah saboda barci da gangan da kauracewa Alkur'ani da zina da liwadi da sauransu.

Kuma daga cikin abubuwan da suke tserarwa daga azabar kabari akwai: kyawawan ayyuka da aka yisu saboda Allah da neman tsari daga Azabar kabarin da karanta suratul mulk da sauran su.
Daga cikin wadanda ake kare su daga Azabar kabari akwai: Shahidi, da wanda yake ribadi (wato daure dawaki domun daukaka hanyar Allah) da mutumin da ya rasu ranan juma'a, da Wanda ciwon ciki ya yi sanadiyyar mutuwarsa, da sauransu.
MUNA ROKON ALLAH YA DATAR DAMU DUNIYA DA LAHIRA

26/01/2026

(HUKUNCE HUKUNCE DA S**A SHAFI MATA)

MAS'ALOLIN JININ HAILA DA NA ISTIHALA. (1)
Ashekara nawa ne mace ke fara haila, sa'annan ta dena? Amsar itace mace takan fara haila ne daga shekara Tara daidai, idan har jini ya fita daga farjinta kafin wannan shekarun to jinin istihala ne (wato jinin ciwo) sannan Babu iyakancewa ga yawan shekarun haila din.

Kwana nawa ne Mafi karanci ga mai haila kafin ya dauke?
Tsawon wuni da dare wato (sa,a 24) in har ya kasa haka to jinin istihala ne.

To kuma kwana nawa ne mafi yawa ga mai haila kafin ya dauke?
Kwana goma sha biyu shine mafi tsawon ga mai haila sannan ya dauke to idan jinin ya wuce haka fa? Ya zama jinin ciwo wato (istihala )

Kwana nawa ne ake samun tazara tskanin haila zuwa haila?
To akan samu kwana goma sha uku tsakanin su, idan har wani jini ya zo kafin cikar kwanukan to ya zama jinin ciwo (istihala)
Kuma mafi yawancin kwanakin tsarki ga mata shine kwana (23) ko (24)

MUNA ROKON ALLAH YA DA TAR DAMU DUNIYA DA LAHIRA AMIN

Marigayi Sheikh Dr Abubakar Giro Argungu Ya Jagorancin Aza Tubalin Ginin Wani Masallacin Anguwar Rijiyar Bandado Argungu...
10/01/2026

Marigayi Sheikh Dr Abubakar Giro Argungu Ya Jagorancin Aza Tubalin Ginin Wani Masallacin Anguwar Rijiyar Bandado Argungu L/G Kebbi State Nigeria Yana Daga Cikin Ayukan Alherin Da Malam Yake Kafin Allah Ya dauki Rayuwar Sa Muna Rokon Allah Ya Saka Wannan Ayukan A Cikin Mizamin Shi Ameeen

10/01/2026

Ga wasu Ibadun nafila da yakamata kasabawa kanka dasu suzama jiki agareka kafin mutuwarka
👇👇👇

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba mu ƙarshe mai kyau, Ya sa mu rasu muna kan gaskiya da imani.Ana Iya Samun Mutum Mai Kirki, ...
30/12/2025

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba mu ƙarshe mai kyau, Ya sa mu rasu muna kan gaskiya da imani.

Ana Iya Samun Mutum Mai Kirki, Amma Daga Baya Ya Sauya Ya Koma Mutum Mara Kirki.
Haka Kuma Ana Iya Samun Mutum Mara Kirki, Daga Baya Ya Tuba Ya Koma Mutum Mai Kirki.
Saboda Haka, Kada A Yi Gaggawar Yankewa Mutum Hukunci, Domin Ba A San Yadda Rayuwar Mutum Za Ta Ƙare Ba. Abin Lura Shi Ne Abin Da Mutum Ya Cika Da Shi A Lokacin Mutuwarsa.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba mu ƙarshe mai kyau, Ya sa mu rasu muna kan gaskiya da imani.

Sheikh Ahmed Tijjani Yusuf guruntum HAFIZAHULLAH

fans

**FALALAR ZAMA A WURIN SALLAH BAYAN AN IDAR**Daga Abu Huraira* (Allah ya ƙara masa yarda) yace: *Manzon Allah ﷺ ya ce:*❝...
29/12/2025

**FALALAR ZAMA A WURIN SALLAH BAYAN AN IDAR*

*Daga Abu Huraira* (Allah ya ƙara masa yarda) yace: *Manzon Allah ﷺ ya ce:*
❝ *Mala’iku suna yi wa ɗayanku *salati (roƙon gafara) muddin yana *zaune a wurin da ya yi sallah, matuƙar bai yi *hadasi* ba (abinda zai warware alwala).*
*Suna cewa: ‘Ya Allah, ka *gafarta* masa. Ya Allah, ka *ji ƙansa*.’ ❞
— *[Bukhari da Muslim]*

*Darasi:*

*Hadisin yana nuna girman lada da falala ga wanda ya zauna cikin tsarki a wurin da ya yi sallah, tare da samun addu’ar mala’iku a gare shi.*

MAFI DARAJA DAGA CIKINKU WAJAN ALLAH! 1. Mafi girman mutane a wajan Allah wanda yafi tsoran Allah2. Mafi daraja a cikin ...
29/12/2025

MAFI DARAJA DAGA CIKINKU WAJAN ALLAH!

1. Mafi girman mutane a wajan Allah wanda yafi tsoran Allah

2. Mafi daraja a cikin mutane Wanda bashi da rowa

3. Mafi daukaka a cikin mutane, wana bashi da yawan surutu

4. Mafi amfani a cikin mutane wanda yake amfanar mutane.

5. Mafi tsaftar mutane wanda yake yiwa mutane kyakyawan zato.

6. Mafi alkhairin mutane wanda ya koyi Alkurani kuma yake koyarwa.

7. Mafi kyawun aiki a wajan Allah shine, kasanya wani cikin farin ciki,

8..Mafi aikin da yafi shine, yin salla akan lokaci.

9. Mafi aikin alkhairi shi ne Biyayya ga iyaye.

10. Mafi aikin da Allah ya fi so, wanda aka dawwama akan sa ko kaɗan ne.

Allah ya sa mu yi abin da yake so, kuma yadda yake so.

WANNAN TUNATARWA CE, AMMA SHIN ZUCIYARKA ZA TA KARƁA?Ya kai bawan Allah…Ka taɓa tsayawa ka tambayi kanka:Me Annabi Muham...
29/12/2025

WANNAN TUNATARWA CE, AMMA SHIN ZUCIYARKA ZA TA KARƁA?

Ya kai bawan Allah…
Ka taɓa tsayawa ka tambayi kanka:
Me Annabi Muhammad ﷺ ya faɗa game da tashin Al-Qiyama?
Shin alamominta labari ne kawai, ko gargaɗi ne gare ni da kai?

Wallahi, Annabi ﷺ bai bar mu cikin duhu ba.
Ya bayyana alamomi, domin mu farka kafin a ce an makara.

MANYAN ALAMOMIN TASHIN AL-QIYAMA

Ya kai bawan Allah…
Annabi ﷺ ya lissafa manyan alamomi guda goma, waɗanda idan s**a fara, babu ja da baya:

– Fitowar Dujjal
– Saukar Annabi Isa (A.S)
– Fitowar Yajuju da Majuju
– Fitowar Rana daga Yamma
– Fitowar Dabba daga ƙasa
– Hayaki (Dukhan)
– Ramin ƙasa a Gabas
– Ramin ƙasa a Yamma
– Ramin ƙasa a Tsibirin Larabawa
– Wuta daga Yemen da za ta tura mutane zuwa Mahshar

Ya kai bawan Allah…
Dukkan waɗannan har yanzu ba su bayyana ba.
Amma idan ɗaya ya fara, sauran za su biyo baya kamar zoben sarka.

ƘANANAN ALAMOMI – WAƊANDA S**A RIGA SU FARU

Ya kai bawan Allah…
Wasu alamomi sun riga sun cika, muna karanta su ne kawai a littattafai:

– Aiko Annabi Muhammad ﷺ
– Rabuwar Wata
– Yawaitar mutuwar sahabbai
– Yaƙe-yaƙe da fitintinu
– Bayyanar ƙarya annabawa
– Buɗe Baitul-Maqdis
– Annobobi da cututtuka

Shin ba abin tsoro ba ne,
abin da Annabi ﷺ ya faɗa ƙarni da ƙarni ya gabata, yau muna gani da ido?

ƘANANAN ALAMOMI – WAƊANDA SUKE FARU A ZAMANI YANZU

Ya kai bawan Allah…
Ka dubi duniya, ka duba kanka:

– Gaskiya ta yi wuya, amana ta ɓace
– Zina ta yawaita, kunya ta ragu
– Giya da riba sun zama ruwan dare
– Jahilai suna magana a addini
– Ƙananan mutane suna jagorantar manya
– Mutane suna fafatawa gina manyan gine-gine
– Lokaci yana raguwa
– Kisan kai yana ƙaruwa
– Ƴa’ya suna bijire wa iyayensu

Ya kai bawan Allah…
Shin wannan ba hoton zamaninmu ba ne?

ƘANANAN ALAMOMI – WAƊANDA SUKE GAB DA FARUWA

– Ƙasar Larabawa ta koma kore
– Zinariya ta fito daga Kogin Furat
– Mutum ya nemi mai karɓar zakka ya rasa
– Salam a yi shi ga wanda aka sani kawai
– Ilimi ya ragu, jahilci ya yi yawa

SAƘO MAI GIRMA

Ya kai bawan Allah…

Address

Mahuta Street

Telephone

+2348129769315

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DARUL HAQ posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your practice to be the top-listed Law Practice?

Share