29/10/2025
Jiya na ji wani kasurgumin makaryaci Dan Bidi'a yana yi wa Ahlus-Sunnah sharri, yana cewa ba su taɓa yin wata lacca mai taken “Son Annabi Muhammad ﷺ” ba.
Wannan ƙarya tasa ta tunatar da ni karatun littafin Ash-Shifā, wanda Sheikh Abdurrazaq Haifan (hafizahullah) yake karantawa. A cikin darussa na 002 da 003, Malamin ya gabatar da karatun mai taken “Ayoyin Ɗaukakar Annabi ﷺ.”
Ina roƙon duk mai son gaskiya da neman ilimi da ya samu lokaci ya saurari waɗannan darussa guda biyu (tsawon sa’o’i biyu kacal). Zai ga yadda Malamin ya yi bayani mai zurfi, cike da ƙauna, ladabi da girmamawa ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam.
Lallai, waɗannan karatun suna ƙara haske ga zuciya, suna kuma ƙarfafa soyayya da biyayya ga Annabi ﷺ, wanda shi ne ginshiƙin addininmu.