27/04/2026
Jama’ar al'ummar karamar hukumar Fagge mai albarka, ina yi muku fatan alkhairi gaba ɗaya.
Ina miƙa godiyata ta musamman bisa irin goyon baya da ƙwarin gwiwar da kuke ci gaba da bani a wannan tafiya. Lallai, da ba ku ba, da wannan tafiya ba za ta samu wannan nasara ba.
Ina ƙara roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saka muku da alkhairi, Ya ba mu nasara, Ya kuma ƙara haɗa kanmu da zumunci a tsakaninmu. Allah Ya ba mu lafiya da zaman lafiya, Ya kuma ba mu ci gaba mai ɗorewa da albarka a ƙaramar hukumar mu ta Fagge.
FAGGE ITACE KAN GABA A MURADUNMU!
Naku,
Hon. Barr. Usman Sa’idu Maikeke