Ihyaa'ussunnah

Ihyaa'ussunnah wannan shafine da aka qirqireshi Don tunatadda kammu da Yan uwammu abunda ya shafi addininmu

12/09/2020

:
Canzawar ruwa da muke Magana akanshi yana da kyau musan abinda ruwa yake da canzawa da shi lura da hukunce-hukuncen kowanne, kamar haka:
- : Idan ruwa ya canza kala ko dandano ko shinshina, saboda inda yake, kamar Jarkasa, Farar kasa, Kanwa, Kainuwa, Gansakuka… duk wadannan idan ruwa ya canza ya yi fari saboda wurin farar kasace ko ya yi Jaa saboda wurin jarkasace ko dandanonshi ya yi gafi saboda wurin kanwace ko tekuce ko wuraran da ake hakar mai, duk wannan canza wad a ruwa ya yi babu abinda ya shafeka zaka yi ibadarka da shi salin-alin alattacciyar ibada.
Kenan waccar Magana da aka yi sai idan ruwan ya canza da wani abu na daban da ba makwancinsaba ta yadda zai iya yuwuwa a rabasu amma a inda yake makwancinsane babu yadda za'a yi ka rabasu.
- : Idan wani abu mai tsarki kamar gishiri ko yaji ko miya ko sabulu ya zuba cikin ruwa amma kwatakwata bai canza ruwanba to wannan ruwan za'a yi ibada dashi kamar yadda bayanai s**a gabata, amma idan sun canza ruwane to wannan rowan ba za'a yi ibada da shi ba, amma za'a yi ayyukan gida da shi, kamar girki wanki kunun-zaki d.s.
- : Idan najasa ta jirkita ruwa ta daya daga cikin abubuwannan uku, to bai halatta a yi anfani da wannan rowan kwatakwata ba za'a yi ibada da shi ba, kuma ba za'a yi wasu ayyuka nadaban da shiba kenan kwararar da shi kawai za'a yi.
Lalle wannan ya nuna mana muhimmacin ruwa da kuma yadda addinin musulunci ruwa shine abinda ba yi za su ibada da shi bai sa musu feturba ko gas domin rahamar Allah ga bayinsa sai ya sanya musu ruwa kuma ya sanya shi ya zama sinadarin rayuwa. Saidai kawai idan mutum bai sami ruwaba a lokacinda zai yi tsarki sai ya yi Istijmari, ko zai yi alwala kuma gashi babu ruwa sai ya yi taimama, kamar yadda bayanansu zasu zo nan gaba.
: Daga wadannan bayanai da s**a gabata zai nuna baka yadda addinin musulunci ya baima ruwa kulawa ya kuma sawwake shi, kuma wannan yana nuna mana yadda ya zama wajibi mu tashi musan hukunce-hukuncen ruwa domin idan mutum bai sani ba sai ya debi ruwan wanki ko kuma ruwan da ya gama wanka da shi bayan ya zama sabulu ya ce zai yi tsarki da shi, domin wasu sun dauka ruwan alwala shi ake bashi wannan hukunce-hukunce amma shi tsarki mutum zai iya yi da ko wanne, alhali abin ba haka bane, Allah ya sawwake amin. Allah Shi ne masani.

002   . Abubuwan da suke canza ruwa har ya zama wannan ba za'a yi ibada da shi ba (kamar alwala, tsarki..) abubuwane gud...
08/09/2020

002 .
Abubuwan da suke canza ruwa har ya zama wannan ba za'a yi ibada da shi ba (kamar alwala, tsarki..) abubuwane guda uku, da zarar ruwa ya canza da daya daga cikinsu to wannan ruwan ba za'a yi ibada dashiba, wadannan abubuwa sune:
(1) Launi: dazarar kalar ruwa ya canza ba yadda aka san ruwanba, ko dai ya canza ya yi ja, ko baki, ko kore…' to wannan ruwan ba za'a yi ibada dashiba.
(2) Dandano: Idan dandanon ruwa ya canza to wannan ruwan ba za'a yi ibada dashi ba.
(3) Shinshina: Hakama duk abinda ya jirkita kanshin ruwa zuwa wani abu daban to wannan ruwan ba za'a yi ibada da shi ba.
Idan ruwa ya canza da yada daga cikin wadancan abubuwa uku kenan wadannan abubuwa sun jirkita shi ta yadda ba zai iya amsa sunan ruwaba, domin ya zama Sobo (Zobo) ko kunu ko ruwan datti, to wannan ruwan ba za'a yi ibada da shiba. Amma idan daya daga cikinsu ya fada cikin ruwa amma bai canza ruwanba ta dayan wadancan fuskoki uku to babu abinda ya sami ruwan za'a yi aiki da shi, kuma za'a ibada da shi. Wannan zai nuna kuskuren da ake yi na idan ansa hannu a ruwa ko mutum ya tara fanfo sai kasa hannu ko kasa kwano ko buta sai ace za'a malalar da ruwan wai bashi da tsarki, ko wata dabba da ake ci (wacce ba ta cin najasa) ta sha, ko kuma dabba ta fada rijiya ko ma mutum sai ace wai za'a kwashe ruwan rijiyar azubar (ko guga kaza) wannan duk bai halattaba a musulunci, duk abinda ka ga ya fada cikin ruwa kuma ka cire shi ka ga babu abinda ya canza rowan kwatakwata cikin wadancan abubuwa uku ka yi shiru da bakinka aci gaba da aiki da ruwa. Allah ne masani

07/09/2020

001- HUKUNCE-HUKUNCEN RUWA

Kada ka manta sallah itace ginshike na biyu daga cikin cikaciikan musulunci guda biyar, itace kuma ginshikin addinin musulunci duk wanda ya tsaida ita to ya tsayar da addini, haka kuma duk wanda yabar sallah to yabar addini. Ita kuma sallah bata zama sallah sai idan an yi alwala, an tsarkaka daga dukkanin najasa an gusar da hadasi da kuma kabasi, wato dukkanin najasar da ta fito daga jiki ita ake kira Hadasi, kamar mutum ya yi: fitsari, bayangida, maziyyi…'' shikuma kabasi shine dukkanin najasar da ta shafi jikinka, ko tufafinka, ko kuma wurin sallah. Gusar da wadannan abubuwa na hadasi da kuma kabasi da aiwatar da alwala, basa tabbata sai da ruwa mai tsarki kuma mai tsarkakewa, wato kenan rowan sai ya cika sharudda biyu, na farko ya zama mai tsarki, na biyu kuma ya zama zai iya tsarkake wani.

07/09/2020

Kafun cewa komai zanso innemi afuwa akan duk abunda za agani badaidaiba muna neman shawara dakuma gyara akan duk abunda mukayi badaidaiba

07/09/2020

Address

Marafa Street Alkaleri
Alkaleri

Telephone

+2348065691778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ihyaa'ussunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Ihyaa'ussunnah:

Share

Category